Ƙasar Amurka ta kai hare-hare kan jiragen ruwan Venezuela

Rundunar sojin Amurka ta ce ta ƙaddamar wasu jerin hare-hare a cikin kwanaki biyu akan wasu jiragen ruwa da ta zargi na safarar miyagun kwayoyi ne a tekun Venezuela inda ta kashe akalla mutum takwas.

Rundunar ta ce hari na farko ta kai shi ne kan wasu jiragen ruwa uku da suka yi jerin gwano suna tafiya a tekun inda ta kashe wadanda ta kira masu safarar miyagun kwayoyi a daya daga cikin jiragen.

Rundunar ta ce hari na biyu kuwa ta kai shi ne a daren sabuwar shekara inda ta kashe mutum biyar.

Masu tsaron tekun Amurka sun ce suna neman wadanda suka tsira, to amma sun ce basu sani ba ko akwai wanda ya tsiran.

Gwamnatin Trump ta kai hare-hare fiye da 30 akan mutanen da ta ke zargi suna safarar miyagun kwayoyi a yankin Pacific da kuma Karebiya tun daga watan Satumbar daya gabata inda ta kashe kusan mutum 120.

You might also like
Leave a comment