Gwamnatin Jihar kano ta shiryawa Yan jaridar yanar gizo Taron karawa juna sani na kwana biyu a Jahar jigawa

Gwamnatin Jihar Kano ta shirya Bitar kwana biyu ga Yan jaridar yanar  gizo a jahar jigawa don  jaddada inganci aikin jaridar yanar gizo bisa gaskiya da da,a afadin  jahar,  inda ta bayyana kafafen yaɗa labaran a matsayin ginshiƙi wajen tafiyar da dimokuraɗiyya.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Kwamaret Ibrahim Abdullahi Waiya, shine ya bayyana hakan a ranar Laraba 14-1-2026 yayin da yake bayani awajen  taron horaswa a Dakin taro na man power development institute dutse  na kwanaki biyu ga mambobin kafafen yada labarai na zamani [Kano Online Media Chapel]

Waiya  yace an shirya horon ne saboda  goyon bayan Gwamnatin Jihar Kano, don basu horo na musamman akan  harkar jaridar yanar gizo.

Waiya ya Kara da cewa  wannan horo, shi ne irinsa na farko ga masu wallafa jaridun intanet a Jihar Kano, inda ya nuna   yadda  Gwamna Abba Kabir Yusuf ke kallon aikin jarida a matsayin Wani  ɓangare na tafiyar da ayyukan dimokuraɗiyya.

Akarshe  Kwamishinan ya yi kira ga ‘yan jaridar masu wallafa labarai ta yanar gizo da su riƙa bin ƙa’idojin aikin da nuna  ƙwarewa da gaskiya wajen tattarawa da yaɗa labarai.

Anasa bangaren  Mukaddashi Babban Sakatare na Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Malam Usman Bello, ya ce gwamnati ta amince da gudanar da taron ne a wajen jihar Kano sakamakon muhimmancin da aikin jaridar yabar gizo ke Dashi.

You might also like
Leave a comment