Gwamnan Adamawa Ahmadu Fintiri ya koma jam,iyyar APC
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar da sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar APC a hukumance.
A jawabin da ya yi wa al’ummar jiha a ranar Juma’a, gwamnan ya ce ya ɗauki matakin ne tare da duka mambobin majalisar zartarwarsa da manyan jiga-jigan jam’iyyar adawa ta PDP, kamar yadda jaridun ƙasar suka ruwaito.
Sauya shekar tasa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da ganin sauya sheƙar wasu gwamnoni da jiga-jigan jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a Nigeria.
Har yanzu dai babu cikakken martani daga shugabannin jam’iyyar PDP na ƙasa dangane da matakin gwamnan.
A baya-bayan nan ne dai Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya kai ziyarar aiki jihar, tare da ƙaddamar da wasu ayyukan da gwamnan ya gabatar, matakin da wasu ke ganin tamkar zawarcin gwamnan ne.