Gwamnatin Neja ta amince da sake buɗe makarantun jihar
Gwamnatin jihar Neja da ke arewa ta tsakiyar Najeriya ta amince da sake buɗe makarantun furamare da na sakandiren jihar.
Cikin wata sanarwa da kwamishiniyar ma’aikatar ilimin furamare da sakandiren jihar, Hajiya Hadiza Mohammed ta fitar ta ce an ɗauki matakin ne bayan tuntuɓar masu ruwa da tsaki kan harkokin ilimi a jihar.
Sanarwar ta ce za a sake bude makarantun jihar ranar 12 ga watan Janairun da muke cikin domin ci gaba da harkokin koyo da koyarwa.
Sai dai sanarwar ta fayyace cewa makarantun da suke wurare masu tsaro ne kawai za a buɗe domin ci gaba da karatu.
Matakin na zuwa ne bayan da jihar Kebbi mai makwabtaka da sanar da sake bude makarantu a ranar 5 ga watan Janairun.
Cikin watan Nuwamba ne dai jihohin suka sanar da rufe makarantun jihohin sakamakon hare-haren da ƴanbindiga suka kai wa wasu makarantun jihohin hare-hare tare da sace ɗalibai.