INEC ta gargadi jama’a kan shafin ɗaukar ma’aikatan wucin-gadi na bogi.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta fitar da sanarwar gargadi ga al’ummar Najeriya dangane da wani shafin intanet na bogi da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke iƙirarin cewa shi ne shafin ɗaukar ma’aikatan wucin-gadin hukumar na shekarar 2026.

INEC ta bayyana cewa shafin ba shi da wata alaƙa da hukumar, tare da jaddada cewa dukkan bayanai da ƙididdiga ko takardun neman aiki da ke cikinsa ƙarya ne kuma an ƙirƙire su ne domin yaudarar jama’a.

Hukumar ta ce tana gudanar da ɗaukar ma’aikata ne kawai ta shafin ta na hukuma mai suna INECPRES.

Hukumar ta shawarci masu neman aikin da su riƙa tantance sahihancin duk wani bayani ta shafukanta na hukuma kuma su guji shafukan da ba su dace ba, tare da kaucewa bayar da bayanan sirri kamar BVN da takardun bayanan mutum ko bayanan asusun banki.

Hukumar ta kuma buƙaci duk wanda ya yi rajista a shafin ta bogi da ya dakatar nan take, ya sake nema ta hanyoyin da INEC ta amince da su.

You might also like
Leave a comment