Ministan harkokin wajen Isra’ila ya ziyarci Somaliland bayan amincewa da ita
Ministan harkokin wajen Isra’ila, Gideon Sa’ar, ya isa birnin Hargeisa, babban birnin Somaliland, inda ya gudanar da ziyara ta farko a hukumance tun bayan da Isra’ila ta amince da ‘yancin kan yankin.
Majiyoyi masu tushe a Somaliland sun shaida wa BBC Somali da kafafen labarai na cikin gida cewa Sa’ar ya sauka a birnin ne a ranar Talata da safe.
A yayin ziyarar, ana sa ran zai gana da shugaban Somaliland, Abdirahman Mohamed Abdullahi, inda shugabannin biyu za su yi jawabi ga manema labarai a fadar shugaban ƙasa.
Wani jami’in diflomasiyya ya bayyana cewa ziyarar na da nufin bunƙasa haɗin gwiwar siyasa da dabaru tsakanin Isra’ila da Somaliland, inda ya bayyana hakan a matsayin mataki na ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.
Har zuwa yanzu, ma’aikatar harkokin wajen Isra’ila ba ta yi wani bayani a fili game da ziyarar ba.
Tun daga shekarar 1991, Somaliland ta bayyana ‘yancinta daga Somalia, amma ba a amince da ita sosai a duniya ba.