murka ta sake kama wani jirgin dakn mai a kusa da tekun Venezuela

Rahotonni na cewa  dakarun Amurka sun sake kama wani jirgin ruwan dakon mai a kusa da gabar tekun Venezuela.

Wani kamfanin kula da sufurin ruwa ya ce jirgin ya yi yunƙurin bi ta wani wuri da rundunar sojin ruwan Amurka ta killace a yankin Venezuela.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da Rasha ta bayar da rahoton cewa Amurka ta saki ma’aikatan jirgin manta biyu da ta kama ranar Laraba a gaɓar Tekun Atalantika.

A baya Amurka ta ce ma’aikatan jirgin za su fuskanci tuhuma.

Kawo yanzu ba a san adadin sauran ma’aikatan jirgin da kuma ƙasashensu ba.

You might also like
Leave a comment