Peter Obi ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Labour a zaɓen 2023, Peter Obi, ya sanar da sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar haɗaka ta ADC.
Obi ya bayyana hakan ne a wani taro da magoya bayansa da shugabannin siyasa suka gudanar a Enugu, babban birnin Jihar Enugu.
Da yake jawabi a taron, Peter Obi ya ce bayan watanni na tuntuɓa da tattaunawa, su da sauran shugabannin yankin Kudu maso Gabas sun yanke shawarar shiga ADC domin haɗa ƙarfi da sauran jam’iyyun adawa.
Ya ce burinsu shi ne “Ceto Nijeriya daga mummunar shugabanci tare da yin duk mai yiwuwa don daƙile maguɗi da murɗiyar zaɓe a shekarar 2027.
Manyan shugabannin siyasa daga sassa daban-daban na ƙasar da wasu tsofaffin gwamnoni da manyan jiga-jigan siyasa da shugabannin siyasar Kudu maso Gabas ne suka halarci taron lamarin da ya nuna yunƙurin ƙarfafa haɗin kan adawa gabanin zaɓen 2027..