Shugaban kasa bola Ahmad tunibu ya amince da tura jakadun nigeria 4 zuwa kasashen waje

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da tura jakadu huɗu daga cikin mutum 68 da Majalisar Dattawa ta tantance tare da amincewa da su a watan Disambar da ya gabata.

 

A cikin sanarwar da mai magana da yawun Fadar Shugaban Ƙasa Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya tabbatar da naɗa Ambasada Ayodele Oke a matsayin jakadan Najeriya a ƙasar Faransa, yayin da Kanal Lateef Are zai kasance jakadan Nigeria a kasar Amurka.

Haka kuma, shugaban ya amince da naɗa Ambasada Aminu Dalhatu, tsohon jakadan Najeriya a Koriya ta Kudu, a matsayin jakadan Najeriya a Birtaniya.

Sanarwar ta kuma ce Usman Isa Dakingari Suleiman, tsohon gwamnan jihar Kebbi, shi ne jakadan Najeriya a ƙasar Turkiyya. Wannan na zuwa ne yayin da ake sa ran Shugaba Tinubu zai kai ziyarar aiki zuwa Turkiyya a mako mai zuwa.

A wata takarda da ya aikawa Ma’aikatar Harkokin Waje, Shugaba Tinubu ya umarci ma’aikatar da ta sanar da gwamnatocin ƙasashen huɗun game da naɗin jakadun, kamar yadda ƙa’idojin diflomasiyya suka tanada.

You might also like
Leave a comment