Gwamnan jahar jigawa umar namadi danmodi ya ware kujerun aikin Hajji 27 ga Malamai a Jihar

A wani  mataki na ƙarfafa jagorancin addini da tabbatar da ingantaccen aikin Hajji,

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya bayar da kujerun Hajji guda 27 ga malamai, inda kowace Karamar Hukuma ta samu kujera ɗaya.

Wannan shiri ya yi daidai da kudurin Gwamna Namadi na ganin an samu nasara da karɓuwar aikin Hajji ga alhazan Jihar Jigawa, ƙarƙashin jagorancin Darakta-Janar na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmad Umar Labbo, kamar yadda Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Habibu Yusuf Babura, ya bayyana.

An zaɓi malamai cikin tsanaki domin su kasance masu ba da shawarwari da koyarwa ga maniyyata, tare da jagorantar su domin tabbatar da cewa sun gudanar da Hajji mai ma’ana da karɓuwa.

Darakta-Janar ya yaba da wannan karamci na Gwamna, yana mai jinjina masa kan goyon bayan da yake bai wa Hukumar ba tare da ƙasƙanci ba, da kuma rawar da yake takawa wajen tabbatar da nasarar gudanar da ayyukan Hajji cikin sauƙi da tsari.

Ya ƙara da cewa, wannan mataki zai sanya Jihar Jigawa cikin jihohin da suka fi kwarewa wajen gudanarwa da kula da harkokin Hajji a faɗin ƙasar nan.

You might also like
Leave a comment