Gwamnan Kano abba kabir yusuf Ya Sauke Shehu Wada Sagagi daga Mukaminsa na Kwamishinan

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sauke Alhaji Shehu Wada Sagagi daga nadinsa a matsayin Kwamishinan Zuba Jari, Kasuwanci da Masana’antu nan take.

Sanawar na  dauke da sahannun   magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa,  a ranar Alhamis 26-3-2026

 

 

 

 

A cewar sanarwar, an umarci tsohon Kwamishinan da ya mika harkokin ma’aikatar ga Daraktan Kasuwanci nan take.

 

 

 

 

 

Gwamna Yusuf ya nuna godiyarsa ga ayyukan da tsohon Kwamishinan ya yi a lokacin da yake kan mulki.

 

 

 

 

Ya yabawa kwamanshinan  bisa irin  gudummawar da yabayar alokacin aikin sa , musamman a fannonin siyasa, addini, kananan da matsakaitan kasuwanci.

 

 

 

 

 

Gwamna ya yi masa fatan samun nasara a ayyukansa na gaba yayin da yake tabbatar wa jama’a cewa gwamnatinsa na ci gaba da jajircewa wajen samar da ayyuka masu inganci da kuma shugabanci nagari a jihar.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Wannan.  nazuwane  a matsayin   wani bangare  na ci gaba da daidaita tsarin gwamnati don ci gaba  mai dorewa.

 

You might also like
Leave a comment